Wa'iyazu billahi: Yan bindiga sun sake kashe Masallata a cikin Masallaci yayin da suke tsakar yin Sallah a jihar Niger


Ana fargaban cewa mutane da dama sun mutu bayan Yan bindiga sun buda wa jama'a da ke Sallah a cikin wani Masallaci wuta da bindigogi a kauyen Ba’are  da ke karamar hukumar Mashegu a jihar Niger. Shafin isyaku.com ya samo.

Rahotanni na nuni da cewa Yan bindigan sun buda wa masallata wuta ne a cikin Masallacin yayin da suka tsakar Sallar Asuba. 

Kwamishinan yansandan jihar Niger Monday Bala Kuryas, ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya ce akalla mutane 9 ne maharan suka kashe a wannan farmaki.

Wannan yana zuwa ne kasa da wata biyu bayan Yan bindiga sun buda wuta kan wasu Masallata a cikin wani Masallaci a karamar hukumar suka kashe mutum 18.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN