Hakikanin yadda yan bindiga suka shiga har gida suka kashe Basarake da jama'ar gari a Zamfara


An harbe wani hakimi mai suna Alhaji Umaru Bawan Allah a wani hari da aka kai a unguwar Gada dake karamar hukumar Maru a jihar Zamfara. 

Daily Trust ta tattaro cewa an kashe wasu mutane biyar a harin wanda ya faru da sanyin safiyar ranar Laraba 

Mazauna yankin sun ce wasu ‘yan bindiga da dama ne suka afkawa al’ummar garin da misalin karfe daya na dare, inda suka shiga gida-gida, suka sace mutane kana suka harbe wasu har lahira. 

Yan ta'addan sun kuma yi awon gaba da wasu mutane da ba a tantance adadinsu ba, da suka hada da mata da kananan yara, wadanda akasarinsu aka kama a lokacin da suke kokarin tserewa. 

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa: 

Duk da haka, tare da hadin gwiwar 'yan banga na yankin da jami'an tsaro an ceto mutanen da aka sace." 

“An gano 'yan bindigan ne a wani wuri kusa da yankin Karakkai. Jami’an tsaro sun taru inda ‘yan banga na yankin suka taimaka wajen tare hanyar. 

"Bayan wani mummunan artabu, 'yan bindigar sun yi bar wadanda aka sace, watakila saboda ba su da yawa." 

Ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Muhammad Shehu, har ya zuwa lokacin hada wannan rahoton. 

Source: Legit.ng 

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN