Duba wani mumunar lamari da ya auku ranar Kirsimeti


Akalla rayuka bakwai sun salwanta yayinda wasu suka jigata a wani mumunan hadarin motan da ya auku ranar Kirismeti a jihar Ogun.

Daily Trust ta ruwaito cewa wata mota kirar Mercedes Benz MarcoPolo ta yi hadari ne a titin Sagamu-Benin-Ore da cikin daren Asabar misalin karfe 12:00.

A cewar rahoton, motar ta tashi daga Ojuelegba da Legas kuma ta nufi kudu maso gabas.

Jami'ar wayar da kan jama'a a hukumar kiyaye hadura FRSC, Florence Okpe, ta tabbatar da aukuwar lamarin a jawabin da ta saki.

Okpe tace mutum 63 ke cikin motar; maza 40, mata 15 da yara takwas.

Jami'ar ta bayyana cewa motar ta kwacewa direban ne yayinda yake kokarin wuce wata motar ba bisa tsari ba.

Okpe tace:

"An duba lafiyar wadanda suka jikkata yayinda aka ajiye gawawwakin wadanda suka mutu a dakin ajiyan gawan asbitin jihar dake Ijebu Ode."
"An tuntubi ofishin yan sandan Odogbolu kuma an mika musu motar da tayi hadari don dauketa daga hanya."

Source: Legit.ng

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN