Duba hotuna, bayanin budurwa da ta lashe gasar sarauniyar kyau na Najeriya


A ranar Juma'a ne aka zaɓi wata matashiya 'yar asalin Jihar Kano da ke arewacin Najeriya a matsayin wadda ta zo ta ɗaya a Gasar Sarauniyar kyau ta kasar.

Ga wasu daga cikin ƙayatattun hotunan matashiyar mai suna Shatu Garko.

Shatu Garko, mai shekara 18, ta doke zaratan mata 18 a bikin da aka gudanar ranar Juma'a da dare a Landmark Centre da ke birnin Legas.

Shatu ce mace ta farko mai hijabi da ta lashe gasar a tarihi kuma wannan ne karo na 44 na gasar wadda ake kira Miss Nigeria a Turance.

Nicole Ikot ce ta zo ta biyu, sai kuma Kasarachi Okoro da ta zo ta uku.

Ta karɓe kambun ne daga hannun Etsanyi Tukura 'yar Jihar Taraba, wadda ta lashe gasar a karo na 43 a 2019.

A cewar masu shirya gasar, wadda ta yi nasara za ta samu kyautar kuɗi naira miliyan 10, da zama a gidan alfarma na shekara ɗaya, da sabuwar mota, da kuma zama jakadiya ta musamman ga wasu kamfanoni.

A shafinta na Instagram, matashiyar ta yi godiya ga waɗanda suka shirya gasar da kuma waɗanda suka ɗauki nauyin wannan gasar.

Ta kuma gode wa jama'a bisa goyon baya da kuma soyayya da aka nuna mata

BBC Hausa






Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN