Da duminsa: Yan bindiga kai hari Kaduna, sun kashe 2, sun sace 50


Akalla mutum biyu sun rasa rayukansu yayinda akayi awon gaba da mutane 50 yayinda yan bindiga suka kai hari Unguwar Gimbiya dake karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna. 

Wani mai idon shaida wanda ya bukaci a sakaye sunansa ya bayyanawa manema labarai cewa wannan hari ya auku ne sa sanyin safiyar Juma'a, 3 ga Disamba, 2021. 

A cewarsa an bindigan sun kai gari gidaje akalla 13 kuma sai da suka kwashe sa'o'in biyu suna diban jama'a. 

Yace: "Sun kai garmaki Ungwan Gimbiya dake Sabo, karamar hukumar Chikun dake Kaduna, sun kashe mutum 2, sun sace 50." 

Wani mazaunin daban, Gideon Jatau, a cewar Daily Trust, yace ba'a taba kai hari irin wannan ba a garin. Yace suna fuskantar lamari sace-sacen mutane amma wannan ya yi munin gaske. 

Yunkurin samu karin bayanai daga bakin Kakakin yan sandan Kaduna, ASP Muhammad Jalige, ya ci tura. 

Source: Legit.ng News 

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN