Da duminsa: Yadda Gwamna Atiku Bagudu, Kayode Fayemi da wasu Gwamnoni 4 suka lallashi Sanatocinsu don jingine zancen gyara sabon kudirin zabe


Yan majalisar tarayya sun fara shirin amfani da karfinsu domin tabbatar da kudirin zabe a matsayin doka, amma wannan yunkurin ya wargaje. 

Daily Trust ta fitar da rahoto cewa wasu Gwamnoni sun shiga cikin wannan magana, hakan ya sa adadin kuri’un da Sanatoci suke bukata ya kara yin kasa. 

Majiya mai karfi tace gwamnonin APC da na PDP sun kira ‘yan majalisunsu, inda su ka bukaci su ajiye batun warware matakin da shugaban kasa ya dauka 

The Nation tace gwamnan jihar Yobe kuma shugaban APC na rikon kwarya, Mai Mala Buni ne ya jagoranci gwamnoni wajen rushe shirin ‘yan majalisar. 

Sauran gwamnonin da suka lallashi Sanatocin da ke da wannan shiri su ne: Kayode Fayemi, Atiku Bagudu, Yahaya Bello, Gboyega Oyetola da Hope Uzodinma. 

Duka gwamnonin ‘yan jam’iyyar APC mai mulki ne kuma su na da ta-cewa a siyasar jihohinsu. 

Legit Hausa

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN