Da duminsa: Duba abin da Gwamnatin jihar Niger ta yi wa Almajirai 104 na jihar Sokoto


Gwamnatin jihar Niger ta mayar da Almajirai 104 zuwa jihar Sokoto ranar Litinin 20 ga watan Disamba. Shafin labarai na isyaku.com ya wallafa.

Amajiran yan shekara 4 zuwa 10 an gano su ne tare da wani Malaminsu su a wata motar Trela a garin Maikunkele, yayin da suke gaf da shiga jihar Niger daga jihar Sokoto.

Malamin ya ce zai kai su makarantar Allo ne da ke Angwan Biri a karamar hukumar Bosso inda yaran za su zauna domin su yi karatun.

Darakta janar na ma'aikatar kula da hakkin Yara, Niger State Childs Rights Agency, Maryam Kolo ta ce babu tausayi kan yadda aka saka yaran a motar Trela a cikin irin wannan yanayin sanyi tun daga jihar Sokoto har zuwa jihar Niger. 

Ta ce an mayar da yaran zuwa jiharsu ta Sokoto ne bisa la'akari da tabbatar da dokar Gwamnatin jihar Niger na hana barace-barace a fadin jihar da kuma ayyukan Almajiranci.

Reported by ISYAKU.COM

Latsa nan ka shiga Group dinmu na Whatsapp domin samun labaranmu kai tsaye

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin aiko labari mu wallafa maka LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu a garinku LATSA NAN 

Domin Korafi/Tuntubemu LATSA NAN

Shafukan sada zumunta

Twitter twitter.com/isyakalabari

Facebook facebook.com/isyakalabari

 

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN