Zuƙi ta malle,ku na yaudarar ƴan Najeriya,Yahaya Bello ga EFCC kan batun N19.3bn


Gwamnatin jihar Kogi ta yi martani kan takardar da hukumar yaki da rashawa tare da hana yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta fitar kan cewa ta mayar da kudi har N19.3 biliyan da gwamnatin ta boye a wani asusun banki zuwa babban kotun Najeriya, CBN.

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, Wilson Uwujaren, mai magana da yawun hukumar ya ce hukumar ta mayar da kudin zuwa babban bankin Najeriya.

Zuƙi ta malle, ku daina yaudarar ƴan Najeriya, Yahaya Bello ga EFCC kan batun N19.3bn

Zuƙi ta malle, ku daina yaudarar ƴan Najeriya, Yahaya Bello ga EFCC kan batun N19.3bn. Hoto daga EFCC Source: Facebook

Amma kuwa, gwamnatin jihar Kogi ta cigaba da musanta boye kudin a wani banki kamar yadda EFCC ta ke zarginta da yi. Jihar Kogin ta ce hukumar so take ta batar da 'yan Najeriya.

Ta sha alwashin cewa za ta dauka matakin shari'a kan hukumar domin wanke sunan gwamnatin ta.

A cewar gwamnatin jihar Kogi, hukumar yaki da rashawan ta fallasa cewa ta na da wata manufa ta siyasa a tattare da ita, Daily Trust ta ruwaito.

A wata takarda da aka bai wa manema labarai a garin Legas, kwamishinan yada labarai da sadarwa na jihar Kogi, Kingsley Fanwo, ya ce gwamnatin za ta shirya martani cikakke ga hukumar "domin tseratar da kanta daga wannan cin fuska da ake yi mata tare da sharri."

"Wannan takardar da hukumar ta fitar wa da manema labarai gaskiya cike ta ke da sharri kuma da kokarin saka jihar cikin lamarin da bata da hannu a ciki," yace.

"Muna cigaba da tsayuwa kan gaskiyar mu na cewa jihar Kogi ba ta da wani asusun banki wanda takardar ke magana a kai. Muna jajanta wa EFCC ganin cewa babban aiki ne rufe karyar da suka fara zabgawa tare da yaudarar da suke yi.

"'Yan jihar Kogi da dukkan 'yan Najeriya su tabbatar da cewa za mu ga karshe wannan al'amarin," ya kara da cewa.

Mun mayar wa da CBN N19.3bn ta albashin Kogi da Bello ya boye, EFCC

A wani labari na daban, hukumar yaki da rashawa tare da hana yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta ce ta mayar da N19.3 biliyan kudin jihar Kogi wanda gwamnatin jihar ta boye zuwa babban bankin Najeriya.

Legit Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN