Yanzu yanzu: Babbar Kotun tarayyar Najeriya ta ayyana Yan bindiga a matsayin "Yan ta'adda"


Wata babbar Kotun tarayya karkashin Mai Sharia Justice Taiwo Taiwo da ke zamanta a Abuja, ta ayyana  Yan Bindiga a matsayin Yan Ta’adda.

Alkalin ya bayar da odan ex parte bayan Gwamnatin tarayya ta gabatar da bukatar haka a gaban Kotun.

Babban jami'i mai gabatar da kara na tarayya a ma'aikatar Sharia na kasa, (DPP) Mohammed Abubakar ne ya gabatar da takardun karar amadadin Gwamnatin tarayya, wanda a ciki Gwamnati ta bukaci Kotu ta ayyana Yan bindigan daji, Kungiyoyin masu aikata miyagun ayyuka a matsayin Yan ta'adda.

A cikin Takardun da aka gabatar a gaban Kotu, wasu Takardun da ke da alaka da harkokin tsaro sun tabbatar da cewa Yan bindigan ne ke da alhakin kashe-kashen bayin Allah, fyade, sace-sacen mutane da sauran ayyukan keta mutunci da haddin bil' adama a yankin arewa maso gabas da arewa maso tsakiyar Najeriya.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN