Meyasa kowace matsala ta tare a yankin Arewa, Attahiru Jega ya caccaki shugbaannin Najeriya


Tsohon shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta, Farfesa Attahiru Jega, yace shugabannin Najeriya ba su da ilimin kasancewa a matakin da suke sam.

Da yake jawabi a wurin lakcar Maitama Sule, wanda kungiyar ɗaliban Arewa SW-CNG ta shirya a Katsina, ranar Litinin, tsohon shugaban INEC ɗin ya alaƙanta matsalolin Najeriya da rashin jagoranci mai kyau.

A rahoton Dailytrust, Jega yace Najeriya ba ta yi dacen shugabanni ba idan ana magana kan gudanar da ayyukan cigaban ƙasa.

Attahiru Jega

Meyasa kowace matsala ta tare a yankin Arewa, Attahiru Jega ya caccaki shugbaannin Najeriya Hoto: punchng.com Source: UGC

Meyasa kowace matsala ta tare a Arewa?

Farfesa Jega, wanda shine shugaban taro, yace matsalar talauci, zaman kashe wando tsakanin matasa, rashin tsaro, rashin zuwa makaranta, auren wuri da sauran matsalolin da suka shafi lafiya duk sun tattaru a Arewa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

This Day ta rahoto Jega yace:

"Duk wasu manyan matsaloli kamar rashin tsaro, auren wuri, matsalolin da suka shafi lafiya, yara masu gararamba a titi, rashin aikin yi duk sun mamaye yankin Arewa."

"Duk wani abu mara kyau, ko wata matsala zaka ga ta fito ne daga arewacin Najeriya, to meyasa haka? Wannan shine babban abin tambaya."

Meyasa muke tunawa da jagororin mu na baya?

Farfesa Jega ya bayyana cewa a halin yanzun sai dai mutanen arewa su cigaba da bikin tuna manyan mutane irinsu, Saradauna, Maitama Sule, Isa Kaita da sauransu.

"Waɗan nan mutanen sun jaogaranci arewa kuma sun kare martabarta, sun tabbatar da Arewa ta cigaba dai-dai karfinta da matsayinsu na shugabanni."

"Yayin da muke tuna gudummuwar waɗan nan bayin Allah da suka shuɗe, ya dace mu tambayi kan mu, wane irin jagoranci muke samu daga Arewa?"

Sheikh Sani Yahaya Jingir yace babu wanda ya isa ya siyar da kuri'un mutane da sunan karba-karba a 2023.

Shehin Malamin ya kira tsarin da wani abu mai kama da caca, kuma a cewarsa mutane kada su yarda da shi kwata-kwata.

Da yake jawabi, Shugaban kungiyar ta NRO, Gidado Mukhtar, ya koka da yadda shugabanci ke rasa ingancinsa, manufa da kuma tasirinsa, ya kara da cewa akwai bukatar a kawo gyara cikin gaggawa.

Da yake karin haske a taron, Farfesa Abdallah Uba Adamu ya ce kasancewar yankin Arewa yana da harsuna kusan 320, ba za a iya hade shi ba sai dai idan mutum ya san mene ne yankin duk da bambancin addini da banbance-banbancensa.

Shi ma da yake nasa jawabin, Bashir Tofa, ya jaddada bukatar Arewa ta tashi tsaye domin yin magana da murya daya, inda ya bayyana kasala, hassada, kiyayya, rashin aikin yi da rashin aiwatar da manufofi a matsayin muhimman batutuwan da ke haifar da barazana.

A cewarsa:

“Mun zabi shugabanni su yi mana aiki amma sun koma bautar da mu. Muna da dubban abubuwan da ba mu san yadda za mu magance su ba.

“Ba mu da hadin kai, ba ma kaunar junanmu. Me zai faru idan babu Najeriya?"

Wani dattijon Arewa, Musa Magami, ya yi kira ga kowa da kowa da su hada kai, yana mai cewa an mayar da masana’antun Arewa zuwa mafi kaskanci saboda rashin kulawa da aka yi shekaru da yawa.

Ya kara da cewa Saudiyya ta taba shiga cikin wannan hali kuma a yau ta hanyar daukar matakan da suka dace suna daya daga cikin kasashen da suka ci gaba a duniya.

Kungiyar ta NRO tana da mambobi sama da 600 da ke da tushe a Kano kuma tana da alaka da wasu kungiyoyi 15 wadanda na agaji ne.

Ana ci gaba da kai hare-hare Arewa

A makon nan ne aka kara samun mummunan harin 'yan ta'adda a yankin Borno, lamarin da ya kai ga mutuwar wani babban jami'in soja.

Daily Nigerian ta rahoto cewa sojojin sun kai hari kan yan ta'addan ba kakkautawa domin daukar fansa, bayan kisan da suka yi wa manyan jami'an soji.

Hakzalika, an samu jerin hare-hare a yankunan Zamfara da Katsina duk dai a cikin 'yan kwanakin nan.

Legit Hausa

Reported by ISYAKU.COM

Domin samun labaran mu ta Whatsapp kai tsaye Latsa Link a kasa

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin Tuntubar mu ko aiko Labari LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu LATSA NAN

Shafin mu na Facebook facebook.com/isyakulabari 

Shafin mu na Twitter twitter.com/isyakulabari 


إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN