Kotun Shariar Musulunci a Kano ta sake hana belin Sheikh Abduljabbar, ta tura shi Kurkuku, duba dalili


Kotun Shari'ar Musulunci dake zamanta a Kofar Kudu a jihar Kano ta sake hana Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara beli bayan watanni da tsareshi, rahoton BBC Hausa.

Muhammad A Mika’il, wanda ke wakiltan Malam AbdulJabbar a kotu ya sake gabatar da bukatar gaban mai Shar'ia Ibrahim Sarki Yola a zaman kotun da aka yi ranar Alhamis, 25 ga Nuwamba, 2021.

Kotu tace za'a yi zama na gaba ranar 9 ga watan Disamba, 2021.

BBC ta rahoto cewa Gwamnatin jihar Kano ta bi umurnin da kotu tayi na cewa a baiwa Malam AbdulJabbar kudi N20,000 don ya sayi litattafai kuma a kawo masa littafin Sahihul Bukhari da Sahihu Muslim.

Kotun Shari'a ta sake hana beli Shehin Malami

A cigaba da garkame Abdul-Jabbar, Kotun Shari'a ta sake hana beli Shehin Malami Hoto: BBC Hausa Source: UGC

Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN