ISWAP ta kashe wani Janar na sojin Najeriya a harin kwanton bauna a Borno


An bindige wani Birgediya Janar har lahira a harin kwantan baunan da yan ta'adda Daular Musulunci a yammacin Afrika ISWAP suka kaiwa jami'an Soji a jihar Borno, rahoton DailyTrust. 

Sabanin shi an hallaka jami'an Sojoji hudu a harin kwantan bautan da ya auku a Bulguma, kusa da garin Askira, a karamar hukumar Askira Uba. 

An tattaro cewa jami'an 28 Task Force Brigade, Chibok, sun tashi daga barikinsu don kaiwa Sojin dake Askira dauki amma aka bude musu wuta. 

Mun kawo muku cewa 'Yan ta'addan ISWAP sun yi musayar wuta da sojoji a wani sansanin soja da ke karamar hukumar Askira/Uba a jihar Borno. 

Wasu mazauna sun ce sun hango mayakan na ISWAP a cikin wani dogon ayarin motocin bindigu a hanyar Ngude zuwa Askira, da sanyin safiyar yau. 

Adamu Saleh ya shaida wa The Sun cewa: “Al’amarin ya yi muni amma ‘yan ta’addan sun janye a yanzu.” 

Mazauna sun yi ikirarin cewa sun kai rahoton zirga-zirgar 'yan ta'addan ga jami'an tsaro amma ba a dauki wani mataki ba kafin wannan mummunar kungiyar ta afkawa garin Askira bayan sa'o'i. Source: Legit Nigeria 

Reported by ISYAKU.COM

Domin samun labaran mu ta Whatsapp kai tsaye Latsa Link a kasa

https://chat.whatsapp.com/CTugsexjJhBCwuOLVzkGrg

Domin Tuntubar mu ko aiko Labari LATSA NAN

Domin zama Wakilinmu LATSA NAN

Shafin mu na Facebook facebook.com/isyakulabari 

Shafin mu na Twitter twitter.com/isyakulabari 


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN