Da duminsa: Yan bindiga sun kai hari Jami'ar Abuja SQ, sun kwashe ma'aikata da 'yayansu


Wasu tsagerun yan bindiga sun kai hari gidajen Malaman jami'ar Abuja (UniAbuja) cikin daren Talata, 2 ga watan Nuwamba 2021 kuma sun yi awon gaba da mutane. Legit Hausa ta tattaro cewa yan bindiga sun dira gidajen ne dake unguwar Giri, hanyar zuwa tashar jirgin sama Gwagwalada, Abuja.

Hakazalika Jami'ar ta bayyana cewa tuni an tura jami'an tsaro domin tabbatar da tsaro a wajen. Jami'ar ta sanar da wannan hari a shafinta na Facebook. 

Tace: "Wasu yan bindiga sun kai hari gidajen ma'aikatan jami'ar Abuja da safiyar nan. Tuni mun tura jami'an tsaro domin kare mutane." 

Mutum nawa aka sace? Jami'ar ta bayyana cewa an yi awon gaba da ma'aikatan jami'ar akalla mutum hudu da iyalansu. "Muna sanar da cewa an sace ma'aikatanmu hudu da yaransu. Muna kokarin tabbatar da cewa sun kubuta. Yau dai ba dadi," jawabin ya kara. 

Source: Legit.ng 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN