Da Dumi-Ɗuminsa: Karar harbe-harbe na cigaba da tashi a gidan yarin Jos



Jaridar Dailytrust ta rahoto cewa yanzu haka ana cigaba da jin karar harbe-harbe a gidan gyaran halin Jos, jihar Filato. 

Rahotanni sun bayyana cewa karar harbe-harben ya fara tashi ne da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar Lahadi. 

A halin yanzun jami'an tsaro sun mamaye baki ɗaya ilahirin yankin, inada suke cigaba da kula da zirga-zirgan mutane a yankin. 

Da muka tuntuɓi kakakin hukumar gyaran hali NCoS reshen jihar Filato, Jeff Longdiem, kan abinda ke faruwa, ya yi alkawarin zai neme mu daga baya. 

Cikakken bayani na nan tafe... 

Source: Legit.ng 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN