Type Here to Get Search Results !

Da Dumi-Ɗuminsa: Karar harbe-harbe na cigaba da tashi a gidan yarin Jos



Jaridar Dailytrust ta rahoto cewa yanzu haka ana cigaba da jin karar harbe-harbe a gidan gyaran halin Jos, jihar Filato. 

Rahotanni sun bayyana cewa karar harbe-harben ya fara tashi ne da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin ranar Lahadi. 

A halin yanzun jami'an tsaro sun mamaye baki ɗaya ilahirin yankin, inada suke cigaba da kula da zirga-zirgan mutane a yankin. 

Da muka tuntuɓi kakakin hukumar gyaran hali NCoS reshen jihar Filato, Jeff Longdiem, kan abinda ke faruwa, ya yi alkawarin zai neme mu daga baya. 

Cikakken bayani na nan tafe... 

Source: Legit.ng 

Post a Comment

0 Comments
* Please Don't Spam Here. All the Comments are Reviewed by Admin.

Top Post Ad

Hollywood Movies