Mai taimaka wa Gwamnan jihar Bayelsa kan harkokin labarai, Bodmas Kemepadei, ya sake tabbatar da cewa shi fa ya yi ridda daga Addinin Kirista ya koma Addinin gargajiya na bautan ''Egbesu ''. Shafin isyaku.com ya ruwaito.
Tun bara ne dai wannan Hadimin Gwamnan ya yi ridda Kamar yadda ya sanar. Ya ce ya fahimci gaskiyar cewa an rude shi ne ya bar Addinin Kakanninsa ya rungumi wani bakon addini.
Kazalika ya kalubalanci abokansa cewa su ma su yi ridda daga Addinin zamani su koma Addinin gargajiya..
Rubuta ra ayin ka