Wani rikici mai zafi tsakanin wasu mutane biyu masu tura amalanke ya yi sanadin rasuwar mutanen biyu a birnin Aba a ranar Talata,
The Nation ta ruwaito. Rundunar yan sandan jihar Abia ta tabbatar da afkuwar lamarin inda ta ce rikici ne ya shiga tsakaninsu har ta kai daya daga cikin masu tura amalanken ya kashe daya.
Kakakin yan sandan jihar Abia, SP Geoffrey Ogbonna, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai NAN a Aba a ranar Laraba cewa fusatattun mutane sun halaka daya daga cikin masu fadan bayan ya kashe abokin aikinsa. Rahoton The Nation ya ce Ogbonna ya gargadi mutane su guji daukan doka a hannunsu idan rashin jituwa ya shiga tsakani.
Shaidan gani da ido ya magantu kan yadda abin ya faru Wani ganau ya shaidawa manema labarai cewa a safiyar ranar Talata ne masu tura amalanken suka fara rikici kan wanda zai dauki kayan da wani dan kasuwa ya siya a kasuwan kusa da makabarta a Aba, Abia.
Ya ce mazan biyu sun yi mummunar fada da muggan makamai suka yi wa juna rauni kan N200 da za a biya idan sun taimakawa dan kasuwar daukan kayansa.
Majiyoyi sun ce mutane sun yi kokarin raba fadan amma masu amalanken sun ki sauraron rokon mai kayan da sauran mutane da ke kokarin yin sulhu.
Shaidan ya ce daya daga cikin masu amalanken ya dabawa dayan wuka a ciki, wuya sa wasu sassan jikinsa yayin fadan, hakan ya yi sanadin mutuwarsa.
A cewarsa, da ya lura cewa dayan mai amalanken ya mutu, ya yi kokarin tserewa amma mutane suka tare shi suka kashe shi nan take.
Source: Legit