Ash sha: Uwargida ta kitsa sace kanta ta bukaci N50.000 kudin fansa a wajen mijinta, duba abin da ya biyo baya


Rundunar yansandan jihar Ekiti ta kama wata matar aure mai suna Sule Nana bayan ta kitsa sace kanta domin ta karbi N50.000 kudin fansa daga wajen mijinta.

Kakakin hukumar yansandan jihar Ekiti ASP Sunday Abutu ya sanarwa manema labarai ranar Laraba a Adi-Ekiti babban birnin jihar.

Ya ce yansanda sun sami kiran gaggawa daga Nana ranar 20 ga watan Nowamba cewa wasu mutane sun sace ta a dajin hanyar Ifaki-Oye-Ekiti kuma sun bukaci a basu N50. 000 kafin su sake ta.

Bayan yansanda sun shiga bincike ne sai suka gano cewa Nana ce ta sace kanta da kanta domin ta karbi kudin daga mijinta saboda wasu bukatunta.

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN