An gano yadda Wike, Tambuwal da Gwamnoni suka raba mukaman PDP a tsakaninsu


Daily Trust ta samu bayanai a game da yadda gwamnonin jam’iyyar PDP suka raba mukaman shugabanni a majalisar gudanarwa na NWC. 

Gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP sun nuna karfinsu a zaben shugabanni na kasa da aka yi, duk da maslaha aka bi wajen fito da sababbin shugabannin. 

Gwamnonin da suka taka rawar gani sosai a zaben sun hada da Ahmadu Fintiri, Bala Muhammed, Samuel Ortom, Seyi Makinde da Aminu Tambuwal.

Haka zalika akwai gwamna Nyesom Wike wanda shi ne ya dage a kan tsige Uche Secondus. 

Yadda zaben mukaman NWC ya kasance 

Gwamnan jihar Benuwai, Samuel Ortom ya taimaka wajen zaman Iyorchia Ayu shugaban jam’iyya. Sanata Ayu da Ortom sun fito ne daga jiha daya. 

An gano Gwamna Nyesom Wike na jihar Ribas, ne ya yi ruwa, ya yi tsaki wajen ganin Sanata Samuel Ayanwu ya zama sakataren jam’iyyar PDP na kasa. 

Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN