Yanzu-Yanzu: PDP ya yi nasarar jawo tsohon gwamnan Oyo da tawagarsa zuwa PDP

J


iga-jigan masu ruwa da tsaki na jam'iyyar Zenith Labour Party (ZLP) a jihar Ondo sun yanke shawarar komawa jam'iyyar PDP, The Nation ta ruwaito. 

An cimma matsayarsu ta komawa jam'iyyar PDP ne a wani taro da aka yi a garin Ondo da shugaban jam'iyyar ZLP na kasa Dr. Olusegun Mimiko. Wannan dai shi ne karo na uku da Mimiko zai sauya sheka zuwa PDP. 

Sauran shugabannin ZLP da suka halarci taron sun hada da tsohon mataimakin gwamnan Ondo Agboola Ajayi; Hon Gboye Adegbenro da tsohuwar kakakin majalisar Ondo Jumoke Akindele. Hakazalika da shugaban ZLP na Ondo, Hon Joseph Akinlaja; Tsohon dan takarar gwamna Banji Okunomo da kuma tsoffin manyan hadiman Mimiko. 

Legit Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN