Tap di Jan: Wata matar aure ta gundule kan mijinta, duba dalili


Rundunar ƴan sandan Ghana reshen yankin gabas ta kama wata mata da ake zargin ta fille kan mijinta bayan sun samu wani saɓani tsakaninsu.

Ƴan sandan Ghana sun tabbatar da kama matar mai shekaru 27.

Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ƴan sandan reshen jihar gabas DSP Enenezer Tetteh ya ce, lamarin ya faru ne a wani ƙauye mai suna My God Villa Tei Global kusa da wani kauyen manoma da ke gundumar Fantekwa a jihar gabas.

Lokacin da yake bayani a tashar rediyo ta Star FM DSP Eebenezer ya ce ana zargin matar mai suna Rache Tettey da datse kan mijinta Lartey Daniel mai shekaru 35 bayan wata gardama da ta shiga tsakaninsu.

Ya ce bayan sun samu labarin ne al'amarin a ranar Lahadi suka tura jami`ansu don gudanar da bincike.

Ya ce sun tarar da gawar a gefe babu kai, mamacin yana sanye da wando ruwan toka da farar riga ya yi rub da ciki jina-jina kan hanyar wata gona.

BBC Hausa

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN