Kungiyar marubutan Arewa a kafofin sadarwar zamani "Arewa Media Writers" ta ziyarci ISYAKU.COM


Kungiyar marubutan Arewa a kafofin sadarwar zamani "Arewa Media Writers" ta ziyarci wani shahararren marubuci kuma dan Jaridar mai shafin labarai na Isyaku.com " a garin Birnin Kebbi.

Daga Kungiyar "Arewa Media Writers"

Kungiyar Marubutan Arewa a kafofin sadarwar zamani "Arewa Media Writers" reshen Jahar Kebbi  ta ziyarci  wani sananne akan harakar Rubutu kuma dan Jarida wato "isyaku Garba zuru" Mamallakin shafin labarau na isyaku.com.

A yayin ziyarar, kungiyar ta tattauna muhimman batutuwa da suka shafi wannan kungiyar, da kuma abubuwan da suka shafi harkar Media,da yanda ya kamata a yi rubutu da kuma taka tsantsan a kan rubutun karya wanda baya da tushe.


Shugaban gidan Jaridar Isyaku.com ya yabawa kungiyar "Arewa Media Writers" sannan ya sha alwashin bada tashi gudummuwa ga wannan kungiya ta hanyar basu horo a kan yanda zasu dauko rahoto da kuma yanda za su yi rubutu a kyauta, da kuma sauran abubuwan da suka shafi kungiya.

Wadanda suka samu damar halartar wannan ziyarar sun hada da:

1. Abubakar Umar G/gaji

State Chairman (AMW)

2. Muhammad Abdulmumini Fana

Secretary General

3. Ibrahim Adamu

Asst Org Secretary

4. Yusha'u Muhammad Nata'ala

Financial Secretary

5. Ibrahim Muhammad

Member.

Abubakar Umar Gwadangaji.

Daga:

Chairman "Arewa Media Writers" reshen jihar Kebbi.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN