Kungiyar Kiristoci, PFN ta bukaci Gwamnati ta kama Malamin Musulunci, Ahmad Gumi


Kungiyar kiristoci na Pentecostal Fellowship of Nigeria, PFN, ta yi kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kama Sheikh Ahmad Gumi. 

PFN ta reshen kudu maso yammacin Najeriya tana so a damke babban malamin addinin musuluncin ne saboda maganganun da yake yawan yi. 

The Guardian tace kalaman da shehin malamin ya yi kwanan nan, inda yace ka da a ayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda ne ya jawo wannan kira. 

Kungiyar kiristocin tace babban malamin ya kamata a fara kamawa da zargin alaka da ‘yan bindiga. 

Jaridar News Digest tace kungiyar PFN ta dauki wannan matsaya a wajen wani taro da ta shirya a garin Legas a ranar Talata, 26 ga watan Oktoba, 2021. 

Archbishop John Osa-Oni ya yi magana Taron ya samu halartar wakilan kungiyar addinin daga jihohin Oyo, Osun, Ondo, Ogun da Ekiti. 

Shugaban kungiyar na reshen kudu maso yamma, Archbishop John Osa-Oni yace akwai alamar tambaya a game da kalaman da ke fitowa daga bakin shehin.

 Archbishop John Osa-Oni yace da a ce Sheikh Ahmad Gumi jagoran addinin kirista ne, da tuni an kama shi. Faston ya na mai nuna akwai son kai a lamarin. 

Da yake jawabi a madadin Pentecostal Fellowship of Nigeria, John Osa-Oni yace ya kamata gwamnatin tarayya ta kama malamin domin a hukunta shi. 

A na sa bangaren, babban faston nan na Legas, Dr. Alfred Martins, ya yi kira ga gwamnati tayi bakin kokarinta wajen kawo karshen matsalar rashin tsaro. 

Legit Hausa

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN