EFCC 'ta kama matar Gwamnan jihar Kano Ganduje' kan zargin rashawa


Hukumar EFCC da ke yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta kama Hajiya Hafsat uwargidan gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje, kan tuhuwar rashawa da zambar fili da ɗanta ya kai kararta.

Wata majiya daga fadar gwamnatin jihar da ta buƙaci a sakaya sunanta ta tabbatar wa BBC lamarin.

Majiyar ta ce jami'an hukumar EFCC ne suka je har Kano suka kuma tafi da "Goggo" kamar yadda ake kiran ta, zuwa Abuja, don amsa tambayoyi.

Amma ya ce tuni aka kammala kuma har ta koma gida.

Tuhumar da aka yi wa matar Ganduje na zuwa ne makonni bayan ƙin amsa gayyatar hukumar ta EFCC da rahotanni a Njeriya suka ce ta yi.

Jaridun ƙasar sun ce ɗan Hafsat Ganduje Abdualzeez Ganduje ne ya kai karar mahaifiyarsa gaban EFCC.

Sannan da safiyar Talata É—in wani babban mai taimaka wa gwamnan Kano kan shafukan sada zumunta Abubakar Aminu Ibrahim, ya wallafa wasu hotuna da ke nuna Hajiya Hafsat Ganduje tana saukowa daga jirgi bayan komawarta gida daga Abuja.

BBC Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN