Da duminsa: An sako daliban makarantar kwalejin FGC Birnin Yauri da yan bindiga suka sace a jihar Kebbi


An sako dalibai da malamai da Yan bindiga suka sace na makarantar Sakandare FGC na Birnin Yauri a jihar Kebbi. Jaridar Daily trust ta wallafa.

An sako daliban ne bayan sun shafe kwana 118 a hannun Yan bindiga. Fiye da dalibai 90 ne yan bindiga suka sace yayin wani farmaki da suka kai lokacin da daliban ke karatu a cikin makarantar.

Ranar Alhamis 17 ga watan Yuni ne yan bindiga kimanin su 150 suka farmaki makarantar Sakandare na FGC Birnin Yauri suka yi awon gaba da dalibai 90 wadanda suka hada da maza da mata da malamai uku ciki har da Mataimakin shugaban makarantar.

Daya daga cikin iyayen daliban da aka sace ne ya shaida wa Jaridar Daily trust. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN