An sako dalibai da malamai da Yan bindiga suka sace na makarantar Sakandare FGC na Birnin Yauri a jihar Kebbi. Jaridar Daily trust ta wallafa.
An sako daliban ne bayan sun shafe kwana 118 a hannun Yan bindiga. Fiye da dalibai 90 ne yan bindiga suka sace yayin wani farmaki da suka kai lokacin da daliban ke karatu a cikin makarantar.
Ranar Alhamis 17 ga watan Yuni ne yan bindiga kimanin su 150 suka farmaki makarantar Sakandare na FGC Birnin Yauri suka yi awon gaba da dalibai 90 wadanda suka hada da maza da mata da malamai uku ciki har da Mataimakin shugaban makarantar.
Daya daga cikin iyayen daliban da aka sace ne ya shaida wa Jaridar Daily trust.