Wasu matasa sun wulakanta wani Pasto bayan sun yi zargin cewa ya saci wayar salula. Shafin isyaku.com ya wallafa.
Sun yi zargin cewa Paston ya saci wayar ne a Unguwar NNPC Mega station kan hanyar Otukpo a birnin Makurdi na jihar Benue ranar 18 ga watan Oktoba. Sai dai shaidu sun kasa tabbatar da satar.
Tuni dai matasan suka yi wa Pasto rauni har jini yana fitowa a fuskarsa.