Yanzu yanzu: Mutum biyu sun mutu bayan ginin Chochi ya rufta wa masu ibada (Hotuna)


Mutum biyu sun mutu bayan ginin Mujami'ar da suke bauta a ciki ya rufta kansu a jihar Taraba ranar Lahadi 11 ga watan Satumba. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.

Lamarin ya faru ne a Mujami'ar Holy Ghost Church da ke garin Abeda Pave a Mazabar  Chachanji da ke karamar hukumar Takun a jihar Taraba .

Mun samo cewa akwai mutane da ba a fayyace adadinsu ba da suka sami raunuka daban daban sakamakon ruftawar ginin yayin da jama'a ke tsakar yin ibada a Mujami'ar.

Rahotanni sun ce ginin ya rufta ne sakamakon ruwan sama da aka yi ta yi a garin.




Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN