Mutum biyu sun mutu bayan ginin Mujami'ar da suke bauta a ciki ya rufta kansu a jihar Taraba ranar Lahadi 11 ga watan Satumba. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.
Lamarin ya faru ne a Mujami'ar Holy Ghost Church da ke garin Abeda Pave a Mazabar Chachanji da ke karamar hukumar Takun a jihar Taraba .
Mun samo cewa akwai mutane da ba a fayyace adadinsu ba da suka sami raunuka daban daban sakamakon ruftawar ginin yayin da jama'a ke tsakar yin ibada a Mujami'ar.
Rahotanni sun ce ginin ya rufta ne sakamakon ruwan sama da aka yi ta yi a garin.