Rundunar yansandan jihar Ondo ta kama wani mutum mai suna Sam Omojola, dan gidan wani mai gidan haya bayan ya kashe wani mai haya a gidansu da ke garin Oke Ijebu a birnin Akure, babban birnin jihar Ondo. Shafin isyaku.com ya ruwaito
Bayan takaddamar ta barke tsakani mai gidan haya da dan haya, sai mai gidan haya ya kira dansa mai suna Omojola a wayar salula ya ce mai haya da suke rigima da shi ya zage shi.
Isowar dan mai gidan haya Omojola ke da wuya sai ya dauki wani katako ya maka wa mai haya a kai. Nan take ya fadi kuma jini ya dinga fitowa a hanci baki da kunne.
An garzaya zuwa asibiti da mai haya, sai dai Likita ya tabbatar da mutuwarsa. Sakamakon haka yansanda suka kama Omojola dan mai gidan haya suka tafi da shi domin gudanar da bincike.