Yanzu yanzu: Dan mai gidan haya ya kashe wani mai haya a gidansu da katako, duba yadda ta faru


Rundunar yansandan jihar Ondo ta kama wani mutum mai suna  Sam Omojola, dan gidan wani mai gidan haya bayan ya kashe wani mai haya a gidansu da ke garin Oke Ijebu a birnin Akure, babban birnin jihar Ondo. Shafin isyaku.com ya ruwaito

Bayan takaddamar ta barke tsakani mai gidan haya da dan haya, sai mai gidan haya ya kira dansa mai suna Omojola a wayar salula ya ce mai haya da suke rigima da shi ya zage shi.

Isowar dan mai gidan haya Omojola ke da wuya sai ya dauki wani katako ya maka wa mai haya a kai. Nan take ya fadi kuma jini ya dinga fitowa a hanci baki da kunne.

An garzaya zuwa asibiti da mai haya, sai dai Likita ya tabbatar da mutuwarsa. Sakamakon haka yansanda suka kama Omojola dan mai gidan haya suka tafi da shi domin gudanar da bincike.

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN