Yan Bindiga Sun Kai Hari Gonar Obasanjo


Yan bindiga sun kai hari tare da sace wasu ma’aikata a gonar tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a garin Kobape da ke jihar Ogun. Rahotanni sun ce maharan sun faki mutanen ne, tare da budewa motarsu wuta, kana daga baya suka yi awon gaba da su. Jaridar Leadership Hausa ta ruwaito.

Ba a bayyana sunayen mutanen da aka sace ba, amma manyan jami’an katafariyar gonar tsohon shugaban kasar ne. Zuwa yanzu babu wani rahoto daga jami’an tsaro kan faruwar lamarin.

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN