Potiskum - Hukumar yan sanda a jihar Yobe ta damke wata matar aure yar shekaru 22, Khajida Yakubu, kan laifin kashe 'yayan kishiyarta uku da guba.
Wannan abu ya faru ne ranar Juma'a a unguwar Makara-Huta dake karamar hukumar Potiskuma a jihar, rahoton Leadership.
Yaran sun sha guban ne cikin Shayin da kishiyar mahaifiyarsu ta shirya musu.
A jawabin da kakakin yan sandan jihar Yobe,ASP Dungus Abdulkarim, ya saki, ya tabbatar da cewa an damketa.
A cewarsa, Matar da kanta ta garzaya da yaran asibiti bayan da suka sha Shayin misalin karfe 9 na safe amma uku sun rigamu gidan gaskiya, saura 1.
Dungus yace:
"Tuni dai yan sanda sun kaddamar da bincike domin gano abinda ya faru domin hukuntata."
Yaran da aka kashe sune; Zainab Alhaji Haruna (7), Ahmed Alhaji Haruna (9), Umar Alhaji Haruna (12), da Maryam Alhaji Haruna (11).
Legit Hausa