Yadda Amarya ta kashe 'yayan kishiyarta 3 da guba a jihar Yobe,


Potiskum - Hukumar yan sanda a jihar Yobe ta damke wata matar aure yar shekaru 22, Khajida Yakubu, kan laifin kashe 'yayan kishiyarta uku da guba.

Wannan abu ya faru ne ranar Juma'a a unguwar Makara-Huta dake karamar hukumar Potiskuma a jihar, rahoton Leadership.

Yaran sun sha guban ne cikin Shayin da kishiyar mahaifiyarsu ta shirya musu.

A jawabin da kakakin yan sandan jihar Yobe,ASP Dungus Abdulkarim, ya saki, ya tabbatar da cewa an damketa.

A cewarsa, Matar da kanta ta garzaya da yaran asibiti bayan da suka sha Shayin misalin karfe 9 na safe amma uku sun rigamu gidan gaskiya, saura 1.

Dungus yace:

"Tuni dai yan sanda sun kaddamar da bincike domin gano abinda ya faru domin hukuntata."

Yaran da aka kashe sune; Zainab Alhaji Haruna (7), Ahmed Alhaji Haruna (9), Umar Alhaji Haruna (12), da Maryam Alhaji Haruna (11).

Legit Hausa

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN