Wani mutum ya gamu da ajalinsa yayin da ya shiga maƙabartar musulmi cikin dare don haƙo gawa


Wani mutum da ba a gano ko wanene ba ya mutu yayin da ya ke yunkurin hako gawa a makabarta da ke Abeokuta, babban birnin jihar Ogun, Premium Times ta ruwaito.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a makabartar musulmi da ke Iberekodo, karamar hukumar Abeokuta ta Arewa na jihar Ogun.

Abimbola Oyeyemi, mai magana da yawun yan sandan jihar Ogun, ya tabbatarwa Premium Times afkuwar lamarin a ranar Laraba.

Amma ya ce ba zai iya tabbatar da abin da ya kashe mutumin ba, ya kara da cewa an kai gawar mutumin dakin ajiye gawa na Abeokuta.

Ya ce:

"Eh, an tsinci gawa a makabartar musulmi da ke kusa da Iberekodo. An tafi da gawar dakin ajiye gawa an fara bincike."

Abin da wasu mutanen garin suka ce game da lamarin?

Muheed Adeniyi, wani shaida, ya ce an tsinci gawar mutumin ne a cikin makabartar a safiyar ranar Lahadi.

A cewarsa, an tsinci gawar mutumin ne kusa da wata kabari da ya riga ya haka domin ciro gawar da ke ciki.

Adeniyi ya ce:

"Babu wanda ya san abin da ya kashe mutumin. Mun ga kayan haka rami a wurin. Ba mu san abin da ya kashe shi ba. Wata kila gawar ne ta kashe shi."

Mazauna yankin sun ce mutumin ya mutu, wasu na ganin fatalwar gawar ce ta kashe shi.

Sheikh Gumi ya faɗawa Fulani yadda za su yi wa kansu gata a Nigeria

Legit Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN