Wani abin birgewa ya sami Sojojin Najeriya kan lamarin ƴan bindiga a Zamfara


Ƴan Najeriya na ci gaba da yaba wa sojojin Najeriya kan luguden wuta da suke yi wa ƴan bindiga da suka addabi arewa maso yammacin Najeriya.

Ƴan Najeriya na yaba wa sojojin ƙasar ne kan labarai da bayanai da ke nuna yadda sojojin ke kashewa da kama ƴan bindiga masu kai hare-hare da satar mutane a jihohin Zamfara da Katsina da Kaduna da Sokoto.

Wata sanarwa da gwamnatin Zamfara ta fitar a ƙarshen mako ta yi ikirarin cewa jiragen yaƙin rundunar sojin saman kasar sun yi luguden wuta kan fitattun sansanonin 'yan fashin daji a jihar da ma kewaye.

Rundunar Sojin Najeriya ta wallafa bidiyo a shafinta na Facebook da ke cewa babban hafsan sojin ƙasar Janar Faruk Yahaya ya kai ziyara a Zamfara.

Ƴan ƙasar sun ta yaɗa hotunan sojojn a kafofin sadarwa na intanet, tare da yaba masu.

Kuma duk da halin takura da matakin toshe layukan sadarwa ya jefa al'ummar Zamfara, ƴan Najeriya da dama sun bayyana cewa kwalliya na biyan kuɗin sabulu tare da nuna matuƙar goyon baya ga sabbin matakan da hukumomin ƙasar suka ɗauka don fatattakar 'yan fashin daji.

Sanata Shehu Sani ɗan gwagwarmaya wanda ya yi suna wajen caccakar gwamnati, a shafinsa na Twitter ya ce:

"Toshe layuka da aka yi a Zamfara na cikin jerin matakan da aka ɗauka na ƙoƙarin murƙushe ƴan ta'adda da suka haɗa da hana haƙo ma'adinai da haramta hawan babura da rufe makaranttu da kasuwanni. Don haka duk wani mataki na kawo ƙarshen ta'addanci abin maraba ne."

Rahotun BBC

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN