Kai jama'a: Duba yada mahaifi ya kashe dansa mai shekaru 2 da tsananin duka da bulala


Wani mutum mai suna Vwede ya lakadawa dansa mai shekaru biyu duka har lahira a Yenagoa, jihar Bayelsa kuma ya tsere, The Nation ta ruwaito.

Lamarin, wanda ya faru ranar Lahadi 26 ga watan Satumba a kan titin Imiringi a Yenagoa, ya jawo Allah wadai daga makwabta da masu rajin kare hakkin dan adam.

An tattaro cewa mahaifin da ake zargi, daga jihar Delta, ya yi wa yaron mai shekaru biyu bulala mai tsanani sannan ya kai shi asibiti a kan hanyar Ruthmore Hotel a Immiringi bayan yaron ya suma.

Sai dai ya tsere bayan ma'aikatan lafiya da ke bakin aiki sun tabbatar masa da cewa yaron da ya kawo asibitin ya mutu.

An kuma tattaro cewa watakila mahaifiyar yaron ta yi watsi da yaron tare da mahaifinsa ne kuma ta gudu bayan ta haihu.

Mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar Bayelsa, SP Asinim Butswat, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce lamarin akwai sarkakiya a cikinsa kasancewar mahaifin ya tsere kuma ba a san inda yake ba a halin yanzu.

Ya ce ba a san ko wanene mutumin ba kuma tun daga lokacin ya tsere, don haka ya dagula yanayin bincike, inji rahoton Daily Trust.

Tuni, lauyoyi mata da wadanda ke da hannu a yakin da ake yi da cin zarafin jinsi a jihar Bayelsa sun nuna fushinsu kan lamarin.

Shugaban Gidauniyar Doka ta Do, Barr Stanley Churchill Aimiekumo, ya ce maigidan da mahaifin ke zaune ya kira gidauniyar don sanar da su game da barnar, inda ya yi ikirarin cewa mahaifin yana azabtar da yaron dan shekara biyu kafin ma ya hallaka shi.

Kodinetan Jiha na gidauniyar Do, Barr. Comfort Itoru, ya ce an kai rahoton lamarin ga ofishin ‘yan sanda na Akenfa kuma mahaifin ya tsere.

Legit Hausa

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN