Matar da ta ce dan da ta haifa mai suna Basiru "Annabi" ne. Matar mai suna Binta diyar Malam Aliyu matar aure ce, sai dai mijinta ya kyale lamarinta saboda bai yarda da ikirarin da matarsa ta yi ba.
Sai dai shafin labarai na isyaku.com ya samo cewa mijin Binta baya goyon bayan ikirarin da Binta ta yi na alakanta dansu mai suna Basiru da annabta ko kasancewa annabi.
A zaman Kutun shari'a ta 1 a Unguwar Nassarawa da ke garin Birnin kebbi ranar Alhamis 2 ga watan Satumba, Alƙali Mu'awiyya Shehu Birnin kebbi ya tura Binta da mahaifinta Aliyu zuwa asibiti domin a tabbatar da lafiyar hankalinsu.
Kotu ta bayar da umarnin cewa a dawo da su Kotu mako mai zuwa domin yanke hukunci bayan sun amsa tuhumar da ake masu a gaban Kotu ranar Alhamis 2 ga watan Satumba.
Reported by ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/EsSeIwnS18mKkhQwHP3mFx
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari