Kwanan baya, kafofin yada labarai sun ruwaito ministan kwadago da aikin yi, Chris Ngige yana cewa Najeriya, Najeriya a matsayinta na kasa mai tasowa, da wuya ta cika ka'idar Majalisar Duniya da kuma kimar Hukumar Lafiya ta Duniya na samar da likita daya ga marasa lafiya 600.
A bangare guda kuma, ministan ya dage kan cewa Najeriya na da isassun likitocin da za su kula da mutane, yana mai cewa matsalar likitocin ita ce ba a turawa da rarraba ma'aikatan kiwon lafiya daidai gwargwado a wuraren da suka dace.
Ya ce yawancin likitocin kasar nan basu son aiki a yankunan karkara, sun zabi yin aikinsu a birane irinsu Abuja, Legas da Fatakwal.
Baya ga kwararrun likitocin cikin gida, Ngige ya ce likitocin da aka horar daga kasashen waje suma suna dawowa Najeriya don yin aiki.
Ministan ya yi ikirarin cewa a yanzu Najeriya tana da likitoci "kusan 4000 da 'yan kai”, inda ya dage cewa rashin kwararrun likitoci na da nasaba da rashin daidaita aikin.
Yace:
“Don haka, kusan kowa ya tafi Abuja, Legas da Fatakwal don zama. Kuma muna da cibiyoyin kula da lafiya na farko 10,000 wadanda aka yi watsu da su kamar yadda aka yi a kidaya ta karshe.”
Abin da alkaluma suka ce
A watan Agustan 2021, Ofishin Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar da rahoton kididdigar shekarar 2020 kan mata da maza a Najeriya.
Daya daga cikin muhimman kididdiga da aka dauka a cikin rahoton shine adadin likitoci a kowace jaha na tarayya (gami da yawan mata daga cikinsu).
Bayanan da Legit.ng ta samu, sun samo asali ne daga Majalisar Likitocin Hakori ta Najeriya.
Manyan jihohi 10 mafiya yawan manyan likitoci (alkaluman 2019)
Lagos - 2561
FCT - 2523
Ribas - 917
Oyo - 772
Edo - 727
Kaduna - 711
Kano - 632
Delta - 554
Anambra - 552
Filato - 538
Sauran jihohin Najeriya
Osun - 536
Enugu - 491
Ogun - 478
Kwara - 446
Borno - 377
Bayelsa - 359
Benue - 332
Cross Riba - 330
Imo - 319
Ondo - 293
Abiya - 289
Gombe - 286
Akwa Ibom - 278
Katsina - 266
Ekiti - 261
Nasarawa - 258
Bauchi - 243
Kogi - 218
Neja - 217
Sokoto - 201
Ebonyi - 184
Adamawa - 147
Kebbi - 144
Zamfara - 137
Yobe - 133
Jigawa - 131
Taraba - 86
Rahoton ya ci gaba da nuna cewa, tun daga shekarar 2019, Najeriya tana da likitoci 6,713 da ba a tantance su a karkashin kowace jiha ba. Adadin likitocin a kasar ya kai 24,640.
Sai dai, wani rahoto na baya-bayan nan da aka baiwa Hukumar Kula da Lafiya ta Najeriya ya bayyana cewa kusan likitoci 35,000 ne ke aikin a Najeriya.
Rahoton ya ci gaba da bayyana cewa, likitocin da ke aiki 35,000 suna cikin jimillar likitoci 80,000 da suka yi rajista da Hukumar Kula da Likitoci ta Najeriya (MDCN).
Wasu da ba sa aiki a Najeriya ana kyautata zaton cewa suna aiki a kasashen waje yayin da kadan daga ciki suka sauya sana'o'i.
Talauci: Rahoto ya nuna 'yan Najeriya miliyan 27 ke samun kudin shiga N100k a shekara
A wani labarin, wani rahoton Kungiyar Kare Hakkin Bil Adama da Tattalin Arzikin Kasa (SERAP) ya ce ‘yan Najeriya miliyan 27 ne ke samun abin da bai kai Naira 100,000 ba a shekara, inji TheCable.
Kungiyar, a ranar Alhamis 2 ga watan Satumba, ta kaddamar da rahoto mai taken ‘Annobar da aka Manta da Ita: Yadda Cin Hanci da Rashawa a bangaren Lafiya, Ilimi, da Ruwa ke jefa 'yan Najeriya cikin talauci.'
A cewar rahoton, ‘yan Najeriya miliyan 56 na fama da talauci kuma 57.205 daga cikinsu galibinsu na dogaro da kansu ne.
Source: Legit.ng