Da Ɗuminsa: Hotunan mummunan ɓarnar da ambaliyar ruwar da ta halaka mutane 3 a Abuja ta yi


A kalla gawarwakin mutane uku ne aka gano a safiyar ranar Litinin a rukunin gidaje na Trademore da ke Lugbe, babban birnin tarayya, Abuja, Premium Times ta ruwaito.

Rahoton na Premimum Times ya ce mazauna unguwar sun ce ambaliyar ruwan ya fara ne a safiyar ranar Litinin bayan ruwan sama da aka yi kamar da bakin kwarya.

Ambaliyar ruwar ya yi sanadin bacin motocci da wasu kayayyakin mutane da dama a unguwar.

Jami'an hukumar kwana-kwana na birnin tarayya Abuja sun isa wurin a safiyar ranar Litinin domin kai wa mutane dauki

A kan samu irin wannan ambaliyar ruwar a unguwar a duk damina na kowanne shekara.



Source: Legit

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN