A kalla gawarwakin mutane uku ne aka gano a safiyar ranar Litinin a rukunin gidaje na Trademore da ke Lugbe, babban birnin tarayya, Abuja, Premium Times ta ruwaito.
Rahoton na Premimum Times ya ce mazauna unguwar sun ce ambaliyar ruwan ya fara ne a safiyar ranar Litinin bayan ruwan sama da aka yi kamar da bakin kwarya.
Ambaliyar ruwar ya yi sanadin bacin motocci da wasu kayayyakin mutane da dama a unguwar.
Jami'an hukumar kwana-kwana na birnin tarayya Abuja sun isa wurin a safiyar ranar Litinin domin kai wa mutane dauki
A kan samu irin wannan ambaliyar ruwar a unguwar a duk damina na kowanne shekara.
Source: Legit