Wasu yan Majalisar dokoki na jihar Nassarawa sun ketare rijiya da baya bayan an buda wa motarsu wuta da bindiga a kan hanyar Awanga da ke jihar Nassarawa. Shafin isyaku.com ya wallafa.
Tsebe ya ce 'Mu uku mun bar garin Akwanga cikin motocin mu, sai dai yayin da muke karasowa kauyen Wowyen da ke kan hanyar Akwanga/Lafia wanda yake kusa da makarantar koyar da yansandan kwantar da tarzoma MOPOL wajen tsaunukan Ende, yayin da muka nufato wajen gadar kauyen, kawi sai na ji harbi a gefe na. Lamari da ya sa gilashin motar ya fashe.
Tabbas wannn harin an yi shi ne domin a kashe ni".
Kakakin rundunar yansandan jihar Nassarawa ASP Ramhan Nansel, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce yansanda sun kama mutum daya dangane da farmakin kuma suna gudanar da bincike.
https://chat.whatsapp.com/EsSeIwnS18mKkhQwHP3mFx
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari