Da duminsa: Direba ya banke dan KAROTA, ya kara wa wandonsa iska


Wani direba da ba a san ko waye ba a jihar Kano ya banke tare da kashe jami'in hukumar kula da lamurran tituna, KAROTA da ke titin BUK a tsakiyar birnin Kano.

Daily Nigerian ta tattaro cewa, direban ya tsere bayan ya banke jami'in KAROTA kuma abokan aikinsa sun yi kokarin cafkarsa amma abun ya gagara.

A yayin da aka tuntubi mai magana da yawun KAROTA, Nabilusi Abubakar, ya tabbatar da aukuwar lamarin inda ya ce an mika gawar jami'in asibitin kwararru na Murtala Muhammad da ke Kano.

Abubakar ya ce ba zai iya kara cewa komai ba game da lamarin saboda hukumar na jiran rahoton aukuwar lamarin ne daga asibitin, Daily Nigerian ta ruwaito.

Ya kara da daukan alkawarin samar da karin bayani bayan an kammala bincike

Legit Hausa

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN