Alƙali Muawiyya Shehu Birnin kebbi, ya bayar da wannan umarni ne a zaman Kotun na ranar 2 ga watan Satumba 2021. Alƙali ya tambayesu cewa ana zarginsu da
1. Hada Baki domin aikata laifi.
2. Tayar da hankalin jama'a.
3. Cin zarafin Addinin Musulunci.
Ya ce " Mako da ya gabata kun gaya wa Kotu cewa dan Binta mai suna Muhammadu Basiru Annabi ne. Har yanzu kuna kan zancen? Binta da Mahaifinta Aliyu sun ce eh"
Sakamakon haka Alƙali ya bayar da umarni cewa a kai su Asibiti a duba lafiyarsu, sai a dawo da su mako mai zuwa domin yanke hukunci.
Mijin Binta ya ki shiga cikin lamarin
Rahotanni da shafin labarai na isyaku.com ya tattaro, sun yi nuni da cewa Binta mahaifiyar Basiru tana da aure. Sai dai mijinta ya nisanta kansa daga wannan lamari. Mun samo cewa sakamakon haka ya zare hannunsa ya kyaleta da yan uwanta cikin wannan matsala.
Mahaifin Binta Malam Aliyu Isah yana goyon Bayan diyarshi
Aliyu Isah, mahaifi ne ga Binta ba mijinta ba kamar yadda muka sami Labarin farko. Yaro da Binta ta haifa jikanshi ne. Sai dai Aliyu ya dage cewa jikanshi Annabi ne.
Hankalin Binta da Mahaifinta a kwance Babu alamar damuwa tare da su.
A zaman Kotu na ranar Alhamis 2 ga watan Satumba, Binta wacce ke sanye da Hijabi mai klar ja da digo fari gaba daya, tana rike da danta Basiru da ta kira annabi. Yana sanye da rigar dinki jampa mai kala shudi mai duhu.
Mahaifinta Aliyu Isah yana sanye da babbar riga da hulla mai kalar ruwan kasa mai haske. Yanayi da ya bayyana a fuskarsu bai nuna damuwa tattare da su ba a zahiri.
Mai gabatar da kara na yansanda Sgt Faruku Muhammad, mai lambar aiki 493010 ya shigar da kara a madadin Kwamishinan yansandan jihar Kebbi kan Binta da Mahaifinta Aliyu.
Reported by ISYAKU.COM
https://chat.whatsapp.com/EsSeIwnS18mKkhQwHP3mFx
Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN
SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA
Facebook.com/isyakulabari