Bayan katse layin tarho duba yanayin da mazauna jihar Zamfara ke rayuwa babu sadarwa


Mazauna jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana halin takura da suka shiga sakamakon katse layukan waya da intanet da hukumomi suka yi. Shafin BBC ya ruwaito.

Hukumomin kasar sun dauki matakin ne da zummar shawo matsalar 'yan fashin daji da ta addabi jihar.

Ɗumbin jama'ar Zamfara ne a yanzu suke kwarara zuwa maƙwabtan jihohi domin kiran abokan hulɗa da 'yan uwa ta wayar tarho, da sauran aikace-aikacen da katse hanyoyin sadarwa ta haddasa a jihar.

Bayanan da ke fitowa daga Zamfara na cewa harkokin banki sun tsaya cak, yayin da hada-hadar kasuwanci ta taƙaita, a wasu lokuta ma 'yan uwa kan shiga zullumi saboda rashin ji daga makusantansu da ke sassan jihar.

Wasu Zamfarawa da BBC ta zanta da su sun bayyana irin wahalar da suke sha tun ranar Juma'a da aka katse sadarwa, kafin su iya kiran waya ko hada-hadar kuÉ—i a bankuna.

A cewar wani mazaunin "tun daga Ɗansadau a ƙaramarar hukumar Maru na tafi Funtuwa a jihar Katsina don na yi hada-hadar kuɗi saboda rashin sadarwa."

Ita ma wata mai sana'a ta intanet da yanzu haka ta yi balaguro zuwa wata jihar, ta ce rashin sadarwar ya yi matuƙar illa ga cinikin da take samu.

"Harkokina na kasuwancin da nake yi yawanci ina yin su ne a soshiyal midiya. Nakan É—ora abun da nake sayarwa a Whatsapp da Facebook, ka ga wannan lamari ya shafi rayuwata sosai tunda ba ni da sabis ma to ta ina zan fara?"

A wani gefen kuma lamarin ya shafi waÉ—anda ke zaune a wajen jihar ta Zamfara amma saboda matsalar sadarwar ba za su iya jin halin da makusantansu ke ciki ba.

Amma duk da haka da dama sun ce idan har matakin katse sadarwar zai taimaka wa hukumomin fatattakar Æ´an fashin daji, to suna maraba da hakan.

Gwamnatin Zamfara ta fitar da sanarwar cewa sojojin Najeriya sun yi luguden wuta a fitattun sansanonin Æ´an fashin dajin da ke faÉ—in jihar

Bayanan hoto, Gwamnatin Zamfara ta fitar da sanarwar cewa sojojin Najeriya sun yi luguden wuta a fitattun sansanonin Æ´an fashin dajin da ke faÉ—in jihar

A ranar Juma'ar da ta gabata ne hukumomi a Najeriya suka katse hanyoyin sadarwa a jihar Zamfara a wani bangare na fatattakar Æ´an fashin daji da suka addabi jihar.

Kuma kwanaki biyu bayan É—aukar mataki ne gwamnatin Zamfara ta fitar da sanarwar cewa sojojin Najeriya sun yi luguden wuta a fitattun sansanonin Æ´an fashin dajin da ke faÉ—in jihar.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN