An damke wasu mata 3 da ke taimaka wa yan bindiga a gandun dajin jihar Katsina (Hotuna)


Rundunar yansandan jihar Katsina ta kama wasu mata uku da ke safarar man fetur ga yan bindiga a cikin gandun dajin jihar.

Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito cewa, Kakakin hukumar yansandan jihar Katsina SP Gambo Isah, ya gabatar da matan ga manema labarai ranar Alhamis 23 ga watan Satumba. Ya ce jami'an yansanda masu yawon sintiri ne suka kama su a hanyar Katsina zuwa garin Jibia.

Wadanda aka kama su ne Dija Umar, 50; Ummah Bello, 45; da Nusaiba Muhammad, 16, dukkansu suna zaune a rukunin gidajen Malali da ke karamar hukumar Katsina a jihar Katsina.



إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN