Ƴan bindiga sun buƙaci a ba su shinkafa a matsayin kuɗin fansa a Sokoto


Ƴan bindiga masu satar mutane sun nemi a ba su shinkafa maimakon kuɗi domin su saki mutanen da suka yi garkuwa da su a jihar Sokoto da ke arewacin Najeriya, kamar yadda Jaridar DailyTrust ta ruwaito.

Wani mazauni garin Sabon Birni na jihar Sokoto ya shaida wa jaridar cewar ƴan bindigar sun saki yarinyar makwabcinsa bayan an kai masu abinci.

Kuma rahotannin sun ce mudun shinkafa 10 aka kai wa ƴan bindigar suka saki yarinyar.

Haka kuma kuma wasu ƴan bindigar sun buƙaci akai masu buhun shinkafa da kwalayen taliya kafin su saki wani direban mota bayan da farko sun buƙaci a ba su miliyan 15.

An haramta cin kasuwanni a jihohin Sokoto da Zamfara da Katsina da Kaduna da Neja, matakin da ake ganin ya jefa ƴan fashin cikin yunwa.

Rahotun BBC

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN