Abin da ya faru da Sheikh Abduljabbar a Kotu


Babbar kotun musulunci ta Jihar Kano da ke arewacin Najeriya ta ki amincewa da bayar da belin Malamin addinin nan Sheik Abduljababr Nasir Kabara.

Cikin wani zama da aka yi a ranar Alhamis, alkalin kotun Mai shari’a Ibrahim Sarki Yola, ne ya ki amincewa da bukatar da Barista Umar Muhammad wanda shi ne ke jagorantar lauyoyin Abduljabbar ya gabatar.

Gabanin fara shari’ar lauyoyin Abduljabbar sun bukaci da a ba su kwafin shari’ar, tare da kira ga masu kara da su gabatar da shaidunsu a zama na gaba domin a fara sauraro.

Alkalin ya dage saurar karar zuwa ranar 14 ga watan October na gobe.

BBC Hausa

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN