Mutane na ta tserewa daga babban birnin Afghanistan Kabul a cikin motocinsu, lamarin da ya jawo cunkoson motoci a kan tituna.
BBC Hausa ta ruwaito cewa an ba da rahotannin cewa 'yan Taliban na hanyoyin shiga birnin amma an bai wa mayakan umarnin kar su yi rikici sannan kar su hana duk mai son fita daga garin
Kamfanin dillancin labaran Reuters da fari ya ruwaito cewa mutane na barin ababen hawansu suna tafiya da kafa zuwa filin jirgin sama.