Yanzu yanzu: Taliban ta kwace mulkin Afghanistan ta nemi gwamnati ta yi saranda, shugaban kasa ya gudu (Bidiyo)


Daga karshe dai mayakan Taliban sun shiga Kabul babban birnin Afghanistan, kuma sun nemi gwamnati kasar ta yi saranda ba da wani sharadi ba.

Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito cewa shugabann kasar Afghanistan Ashrif Ghani ya tsere zuwa kasar Tajikistan inda ake kyautata zaton ya sami mafaka.

Wannan yana faruwa ne bayan kasar Amurka tare da takwarorinta sun janye sojinsu da suka girka har tsawon shekara 20 bayan mumunan harin 911 a 2001 kan kasar Amurka da aka zargi Osama bin laden da kitsawa tare da marawar Taliban da ke da mazauni a Afghanistan.

Bidiyon yadda Taliban suka shiga Birnin Kabul:

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN