Rundunar yansandan jihar Niger ta kama wasu mutane hudu bisa zargin aikata fashin daji a karamar hukumar Rafi, kuma suka kama su da bindigogi kirar gida a hannunsu. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.
Kakakin hukumar yansandan jihar Niger DSP Wasiu Abiodun, ya sanar wa manema labarai ranar Litinin 23 ga watan Agusta cewa an kama su ne a garin Kagara.
Ya ce wadanda aka kama sun hada da Shehu Usman, 21, Idris Ado, 20, Nasiru Dogo a.k.a Badari, 21, da Umar Yahaya,21, dukkansu a sansanin Fulani da ke kusa da kauyen,Garu -gabas a karamar hukumar Rafi ranar 16 ga watan Agusta.
Ya ce wadanda aka kama sun gaya wa yansanda lokacin bincike cewa sun saci shanaye a kauyukan Garun-gabas da Garun-dangana