'Yan sanda da sojoji sun tsananta sintiri ta kasa da jiragen sama a Zamfara


Yan sandan jihar Zamfara da wasu jami'ai daga hukumomin tsaro da suka hada da sojoji sun tsananta sintirin sama da kasa a yankin Gusau zuwa titin Tsafe zuwa Yankara dake karamar hukumar Tsafe ta jihar. Jaridar legit ta wallafa.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa, wannan na kunshe ne a wata takarda da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan jihar, SP Muhammad Shehu ya fitar a Gusau.

Cikakken bayanin jami'an tsaro

Akwai rahotannin sirri da suka bayyana cewa 'yan bindiga na barazanar kai hari wasu yankunan karamar hukumar Tsafe dake jihar.

Rundunar tare da hadin guiwar wasu hukumomin tsaro ballantana sojojin sun tsananta tsaro a Tsafe da kewaye domin baiwa dukiyoyi da rayuka tsaro,"'yan sandan suka ce.

Ana kira ga jama'a da su kwantar da hankalinsu tare da ci gaba da ayyukan su.

Ana karawa da kira ga jama'ar yankunan da su samar da ingantattun bayanai ga hukumomi na ayyukan 'yan bindigan domin daukar mataki," yace.

إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN