Yadda masu ibada suka bijirewa rusau kan Mujami'arsu ta Ekklesiyar Yan uwa a jihar Borno


Yan kwanaki da suka gabata, Gwamnatin jihar Borno ta rushe Mujami'ar Ekklesiyar Yan’uwa na Najeriya (EYN) a birnin Maiduguri na jihar Borno. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.

An yi zargin cewa jami'an Borno Civilian task force da ke aiki tare da hukumar Borno Geographic Information Service (BOGIS) sun kashe wani mai zanga zanga dangane da rasau da aka yi wa Mujami'ar da ke shiyar Moduganari a birnin Maiduguri.




Rahotanni sun ce Gwamna Zulum ya bayar da umarnin cewa a gudanar da bincike kan zargin kisan.

Sai dai an sami bayyanar wasu hotuna a shafukan yanar gizo, wanda ke nuna masu ibada na Mujami'ar suna gudanar da ibadarsu a harabar rusashshen Mujami'ar. Wasu suna zaune a kan kujerun roba wasu har a kan rusassun bulo na Mujami'an suka zauna, yayin da Malamin Mujami'ar ke gabatar da addu'oi.




إرسال تعليق

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

أحدث أقدم

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN