Wasu matsafa sun yi wa yar shekara 50 fyade, suka kasheta suka cire idanu da al'aurarta


Wasu matsafa sun kashe wata mata mai shekara 50 mai suna Mrs. Patience Komone, a garin Umeh da ke karamar hukumar Isoko ta yamma a jihar Delta.

Shafin isyaku.com ya samo cewa bayan kashe wanan mata, matsafan sun jefar da gangan gawar jikinta bayan sun cire idanunta da al'aurarta.

Matar wacce  aka fi sani da suna Pat, yar asalin garin Otughievwen ne da ke karamar hukumar Ughelli ta yamma, iyalinta sun yi shelar  cewa ta bace tun ranar Talata 27 ga watan Yuli bayan ta bar gida zuwa  garin Umeh inda take zuwa yin sarin Barkono da kayan miya kuma take sayarwa a hanyar Sapele.

Kwamishinan yansandan jihar Ari Muhammed Ali ya tabbatar da haka ranar 4 ga watan Agusta, ya ce an gano gawarta bayan ta fara rubewa a daji ranar Talata, bayan yansanda sun kama wani dan acaba mai suna  Onoriode Simon Akpoavirhi mai shekara 25 wanda shi ne ya dauke ta kan babur ranar da ta bace.

Ya gaya wa yansanda lokacin bincike cewa tare da hadin baki da wani mai gyaran takalma ne mai suna Akpoghene Shoemaker suka kashe matar bayan sun yi mata fyade. Ya ce sun kasheta ne da adda.

Ya ce wani mutum ne mai suna Lucky Daniel da ke garin Ohoro ya biya su N100,000 kuma ya ce su kawo masa sassan jikin dan adam wanda suka hada har da idanu da al'aura.




Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN