Wa da kani sun kashe wani mutum suka cire zuciyarsa suka sayar N15,000, duba dalili


Jami'an yansandan jihar Osun sun kama wasu wa da kane Faseun Afolabi da Fadare Afolabi, tare da wasu mutane hudu bisa zargin kashe wani mutum kuma suka cire zuciyarsa suka sayar da shi a kan Naira dubu goma sha biyar.

Kwamishinan yansandan jihar Osun Olawale Olokode, ya gaya wa manema labarai cewa ranar 24 ga watan Agusta, wata mata ta yi kara wajen yansanda cewa ba a gan danta  mai suna Fasesan Ayoade Moses, mai shekara 35, bai dawo batun lokacin da ya je wajen aiki.



Ya ce binciken yansanda ya kai ga kama wani mai suna Faseun Afolabi. Ya gaya wa yansanda masu bincike cewa shi  ne, tare da abokansa su biyu masu suna Fadare Afolabi, tare da dan uwansa, da kuma Taiwo suka aikata barnar.

Yansanda na ci gaba da gudanar da bincike

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN