Jami'an yansandan jihar Osun sun kama wasu wa da kane Faseun Afolabi da Fadare Afolabi, tare da wasu mutane hudu bisa zargin kashe wani mutum kuma suka cire zuciyarsa suka sayar da shi a kan Naira dubu goma sha biyar.
Kwamishinan yansandan jihar Osun Olawale Olokode, ya gaya wa manema labarai cewa ranar 24 ga watan Agusta, wata mata ta yi kara wajen yansanda cewa ba a gan danta mai suna Fasesan Ayoade Moses, mai shekara 35, bai dawo batun lokacin da ya je wajen aiki.
Ya ce binciken yansanda ya kai ga kama wani mai suna Faseun
Afolabi. Ya gaya wa yansanda masu bincike cewa shi ne, tare da abokansa su biyu masu suna Fadare
Afolabi, tare da dan uwansa, da kuma Taiwo suka aikata barnar.
Yansanda na ci gaba da gudanar da bincike