Shugaban kasar Afghanistan ya gudu zuwa kasar Tajikistan saura kiris Taliban ta kama birnin Kabul


Shugaban kasar Afghanistan Ashrif Ghani ya fice daga kasar Afghanistan zuwa makwabciyar kasar Tajikistan yayin da saura kiris mayakan Taliban su kama
Kabul babban birnin Afghanistan kamar yadda wani babban jami'in gwamnati Abdallah Abdallah ya sanar. Shafin labarai na isyaku.com ya ruwaito.

Wannan yana zuwa ne bayan mayakan Taliban sun kewaye Birnin Kabul bayan sun kama Larduna 26 daga cikin 34 na kasar a kasa da mako biyu kacal.

Mun samo cewa Kakakin Taliban ya ce sun ba mayakansu umarnin cewa kada su cutawa kowa. Ya ce kuma za a bar duk wanda ke son ficewa daga birnin ya yi haka cikin sauki. Ya ce Taliban za ta shiga birnin ne domin ta hana sace sacen dukiyar jama'a da mayar da doka da oda a cikin Kabul. 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN